
Rukuni na biyu na yan Najeriya da aka shirya dawo da su gida daga kasar Afrika ta Kudu sun sauka a Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammad dake Lagos.
Mutanen su 66 da suka sauka a filin jirgin saman da misalin karfe 08:50 na daren ranar Laraba na daga cikin waɗanda suka amfana da shirin da shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince a aiwatar da shi na dawo da yan Najeriya dake a ƙasar ta Afrika ta Kudu ya zuwa gida tun bayan da zanga-zangar ƙyamar baƙi ta barke a ƙasar.
A ranar 11 ga watan Yuni ne rukunin farko na masu dawowa gida su 258 suka iso Najeriya a cikin jirgin saman kamfanin Air Peace da aka yi shata.
Dipo Onabowale shugaban Lagos a hukumar NiDCOM dake lura da yan Najeriya mazauna ƙasashen waje ya ce ya shugaban kamfanin jiragen sama na Value Jet Kunle Soname shi ne ya taimaka wajen ganin an samu nasarar kwaso mutanen.
Onabowale wanda ya wakilci, Abike Dabiri-Erewa shugabar hukumar ta NiDCOM ya yabawa shugaban ƙasa Tinubu saboda sahalewar da ya yi a gudanar da aikin kwaso mutanen.’

