Falana Ya Buƙaci Tinubu Ya Amince Da Daukar Masu Gadin Dazuka 1,000 a Borno


Babban Lauyan Najeriya (SAN), Femi Falana, ya buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da ɗaukar masu gadin dazuka 1,000 aiki a Jihar Borno domin ƙarfafa matakan yaƙi da rashin tsaro.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, Falana ya ce ya kamata gwamnatin tarayya ta faɗaɗa wasu matakan tsaro da ta aiwatar a Jihar Oyo zuwa Borno.

Ya bayyana cewa sama da mutane 415 da suka haɗa da ɗalibai da sauran fararen hula har yanzu suna hannun masu garkuwa da mutane da ’yan ta’adda a wasu dazukan jihar.

Falana ya kuma buƙaci a tura babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Borno domin nuna goyon baya ga al’ummar jihar.

Haka kuma, ya jaddada cewa masu gadin dazukan da za a ɗauka aiki dole ne su samu horo da kayan aiki masu inganci domin su iya tunkarar ’yan bindiga da ’yan ta’adda masu ɗauke da muggan makamai.

Ya ce aiwatar da waɗannan matakai zai taimaka wajen ƙarfafa tsaro da kuma dawo da amincewar jama’a ga ƙoƙarin gwamnati na kare rayuka da dukiyoyi.

More from this stream

Recomended