Amurka Ta Kai Sabbin Hare-hare a Kudancin Iran



Amurka ta tabbatar da cewa ta kaddamar da sabbin hare-haren sojin sama a kudancin Iran a ranar Litinin, inda ta ce ta nufi wuraren harba makamai masu linzami da kuma jiragen ruwa da ake zargin suna ƙoƙarin kafa nakiyoyi a teku.

Rundunar sojin Amurka ta Tsakiya (CENTCOM) ta bayyana hakan cikin wata sanarwa da kakakinta, Kyaftin Tim Hawkins, ya fitar, inda ta ce an gudanar da harin ne domin kare sojojinta daga barazanar da Iran ke haifarwa.

Sanarwar ta ce Amurka na gudanar da matakan kariya ne a ƙarƙashin tsarin “kai wa kai farmaki don kare kai,” yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin tsagaita wuta a yankin.

A gefe guda, rundunar juyin juya halin Iran (IRGC) ta zargi Amurka da keta yarjejeniyar tsagaita wuta, tana mai cewa ta harbo jirgin leƙen asirin Amurka tare da harba wasu jiragen yaƙi da suka shiga sararin samaniyar Iran.

Iran ta kuma bayyana cewa tana da ‘yancin ɗaukar matakin ramuwar gayya kan duk wani hari da Amurka ta ce ya sabawa yarjejeniyar tsagaita wuta.

More from this stream

Recomended