Kotu Ta Yanke Wa Wata Mata Hukuncin Shekaru Ashirin Kan Safar Harsasan AK-47



Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke wa wata mata mai shayarwa, Halima Haliru Umar, hukuncin daurin shekaru ashirin a gidan yari bayan ta amsa laifin mallakar harsasan bindigar AK-47 ba bisa ka’ida ba.

Hukumar tsaro ta DSS ce ta gurfanar da Halima a gaban kotu kan tuhume-tuhume huɗu masu alaƙa da ta’addanci da mallakar harsasai. Kotun ta same ta da laifi a tuhume-tuhume biyu bayan ta amsa laifin.

Mai shari’a Hauwa Yilwa ta ce kotun ta gamsu da hujjojin da masu gabatar da ƙara suka gabatar da kuma amincewar wadda ake tuhuma da laifin.

Kotun ta yanke mata hukuncin shekaru ashirin kan tuhume na uku da kuma shekara guda kan tuhume na huɗu.

Lauyan wanda ake tuhuma ya roƙi kotun ta sassauta hukuncin, yana mai cewa Halima ba ta taɓa aikata laifi ba a baya kuma tana da jariri mai shekara ɗaya da aka kama tare da ita.

Takardun kotu sun nuna cewa Halima ‘yar ƙaramar hukumar Faskari ce a jihar Katsina, kuma ana zarginta da jigilar harsasai guda dari uku da biyu tsakanin Barkin Ladi da Jos ta Arewa a jihar Filato.

Jami’in DSS Fahad Tahir ya shaida wa kotu cewa bincike ya nuna wani mutum mai suna Sani ne ya ba ta umarnin zuwa Zariya da Jos domin karɓo harsasan kafin jami’an tsaro su kama ta tana ɗauke da su.

More from this stream

Recomended