Uba Sani Ya Biya Diyyar Kuɗi Ga Wadanda Ayyukan Tituna Suka Shafa A Kaduna


Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya fara rabon diyyar kuɗi ga mazauna yankin Basawa da za su rasa kadarori sakamakon aikin gina titin Hunkuyi–Unguwan Rimi–Basawa da zai haɗa ƙananan hukumomin Kudan da Sabon Gari.

Gwamnan, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar Kaduna, Dakta AbdulKadir Mu’azu Meyere, ya wakilta, ya ce gwamnatinsa tana aiwatar da ayyukan raya ƙasa ne tare da kare haƙƙin al’umma. Ya bayyana cewa an tantance duk kadarorin da aikin zai shafa cikin gaskiya domin tabbatar da cewa kowa ya samu diyya cikin adalci.

Uba Sani ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta riga ta biya biliyoyin nairori a matsayin diyya ga dubban mutanen da manyan ayyukan tituna da magudanan ruwa suka shafa a faɗin jihar.

More from this stream

Recomended