Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa ficewarsa daga jam’iyyar ADC tare da Peter Obi ba ta da nasaba da sabani tsakaninsu da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar.
Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata hira da gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce sun yanke shawarar barin jam’iyyar ne bayan sun gano wasu matsalolin cikin gida da ka iya hana ADC tsayar da ’yan takara a zabuka masu zuwa.
A cewarsa, “Peter Obi da kansa ya yanke shawarar barin ADC ba saboda muna fada da Atiku Abubakar ko wani ba. Mun bar jam’iyyar ne saboda akwai wasu matsaloli da muke ganin suna da wahalar warwarewa.”
Ya kuma ce har yanzu ba a tabbatar ko jam’iyyar za ta iya tsayar da ’yan takara nan gaba ba.
Kwankwaso ya jaddada cewa siyasa wasa ce kawai, don haka bai dauki takara a matsayin gaba tsakanin ’yan siyasa ba.
Ya tuna cewa a zabukan fidda gwani na baya ya taba fafatawa da Atiku da wasu ’yan siyasa ba tare da wata matsala ba, yana mai cewa, “Ba na fada da kowa, kuma ba na sa ran wani ya yi fada da ni.”
Kwankwaso Ya Bayyana Dalilin Ficewarsa Daga ADC

