Ƴan Majalisar Wakilai 17 Sun Sauya Sheƙa Daga ADC Zuwa NDC

Jimillar ’yan majalisar wakilai 17 sun sauya sheƙa daga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) zuwa Nigeria Democratic Congress (NDC).

Mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu, ne ya bayyana hakan yayin zaman majalisar na ranar Talata, inda ya karanta wasiƙun da suka tabbatar da sauyin jam’iyyar da ’yan majalisar suka yi.

Sauyin ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa a ƙasar, lamarin da ke iya yin tasiri a harkokin majalisar wakilai.

More from this stream

Recomended