
Kasa da sa’o’i 24 bayan ta sanar da buɗe mashigar ruwan Hormuz kasar Iran ta sanar da sake rufe mashigar ruwan kan abinda ta kira rashin cika alkawarin da kasar Amurka ta yi a yarjejeniyar da su ka cimma ta tsagaita wuta.
Mai magana da yawun rundunar soja ta Khatam al-anbia ya zargi kasar Amurka da aikata fashin jiragen ruwa ta hanyar fakewa da cewa ta hana jirage shiga ko fita daga Iran.
A farkon makon nan ne kasar Amurka ta sanar da fara hana jiragen ruwa shiga ko fita daga tashoshin jiragen na kasar Iran.
Ƙasar ta Iran ta ce matuƙar ba za a bar jiragen ruwanta su shige ta mashigin ba to kuwa babu jirgin wata ƙasa da zai wuce.
Mashigar ruwan Hormuz dake tsakanin ƙasar Iran da Oman na da muhimmanci gaske duba da yadda kaso da kusan lita miliyan 25 na ɗanyen man fetur ke wucewa ta ciki a kowace rana.

