Atiku Ya Ziyarci Kwankwaso A Abuja

Jagoran adawar Najeriya, Atiku Abubakar, ya kai ziyara ga jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, a gidansa da ke unguwar Maitama a Abuja.

Ziyarar na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gudanar da babban taron jam’iyyar haɗaka ta ADC, wadda duka shugabannin siyasar biyu ke cikinta.

Har zuwa yanzu, ba a bayyana abin da suka tattauna ba, sai dai ana hasashen cewa ziyarar na da alaƙa da batutuwan siyasa.

More from this stream

Recomended