Kotu Ta Ba EFCC Izinin Kama Tsohuwar Minista Sadiya Umar Farouq

Wata kotu a Abuja ta amince wa Hukumar Yaƙi da Masu Yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta’annati (EFCC) ta kama tsohuwar ministar jin ƙai, Sadiya Umar Farouq.

Hukumar EFCC na zargin tsohuwar ministar da hannu a badaƙalar kuɗaɗe da suka haɗa da dala miliyan 1.3 da kuma naira miliyan 746.6 na ma’aikatar da ake zargin an wawure.

A wani saƙo da EFCC ta wallafa a shafinta na X, ta bayyana cewa mai shari’a Jude Onwuegbuzie ya kuma bayar da umarnin kama sakataren ma’aikatar, Bashir Nura Alkali.

Hukumar ta ce matakin ya biyo bayan gazawar waɗanda ake zargin wajen gurfana a gaban kotu a ranar Alhamis.

Lauyoyin waɗanda ake ƙarar sun nemi a ba su uzuri, inda suka ce rashin lafiya ne ya hana Sadiya halartar kotun, amma kotu ta ƙi amincewa da buƙatar.

EFCC ta ƙara da cewa ta shigar da ƙarar tun ranar 15 ga watan Disamba na shekarar 2025, amma ba a samu damar isar da sammaci ga waɗanda ake zargin ba domin su bayyana a gaban kotu.

Sadiya Umar Farouq ta taɓa rike muƙamin ministar jin ƙai a lokacin gwamnatin marigayi tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, kafin daga bisani ta auri tsohon babban hafsan sojin saman Najeriya, Air Vice Marshal Sadiq Abubakar.

More from this stream

Recomended