Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam ta Amnesty International a Najeriya ta bayyana cewa an kashe mutane 20 tare da sace aƙalla wasu 30 a yankin Mafa da ke jihar Borno.
A cewar ƙungiyar, waɗanda aka kashe a ranar Talata 31 ga watan Maris 2026, ƴan gudun hijira ne maza da mata da ke rayuwa a cikin daji. Rahoton ya ce an kashe su ne yayin da suka fita neman itacen girki.
Amnesty International ta kuma ce akwai wasu aƙalla 30 da aka yi garkuwa da su a harin.
Ƙungiyar ta ƙara da cewa daga cikin waɗanda aka kashe, akwai waɗanda aka yanka, yayin da wasu kuma aka harbe su da bindiga.
Rahotanni sun nuna cewa mutanen sun dade suna fuskantar barazana daga ƙungiyar Boko Haram, lamarin da ya tilasta musu barin muhallansu domin tsira.
An Kqshe Mutane 20, An kuma Sqce 30 A Harin Mafa – Amnesty International

