El-Rufai Ya Sake Gurfana A Gaban Kotu Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa Bayan Rasuwar Mahaifiyarsa

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya sake gurfana a gaban Babbar Kotun Jihar Kaduna a ranar Talata, bisa tuhume-tuhumen da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta shigar a kansa.

Ana tuhumar El-Rufai da laifuka da suka haɗa da amfani da muƙami ba bisa ƙa’ida ba, damfara, da bai wa wasu dama fiye da yadda ya kamata, tare da wasu zarge-zargen da suka shafi harkokin kuɗi.

Ya bayyana a gaban kotun ne bayan da ICPC ta sake shi daga tsare da ta yi masa na sama da wata guda. Sakin nasa ya biyo bayan rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Ummar El-Rufai, a birnin Cairo na ƙasar Masar.

Bayan kammala shari’ar a Babbar Kotun Jihar, ana sa ran za a miƙa shi zuwa Kotun Tarayya da ke Kaduna domin ci gaba da shari’ar, inda za a fara sauraron buƙatar belin da ya gabatar.

Rahotanni sun nuna cewa za a duba batun belin nasa cikin gaggawa, la’akari da nauyin tuhume-tuhumen da ake yi masa.

More from this stream

Recomended