
Ɗan takarar gwamnan jihar Kano ƙarƙashin jam’iyar APC a zaɓen 2023,Dr. Nasir Yusuf Gawuna ya sanar da ficewarsa daga jam’iyar APC.
Sanarwar fitarsa daga jam’iyar na kunshe ne a cikin wata wasika dake ɗauke da kwanan watan 29 ga watan Maris da ya aikewa da shugaban jam’iyar APC na mazaɓar, Gawuna dake karamar hukumar Nassarawa ta jihar Kano.
A cikin wasikar tasa Gawuna ya bayyana cewa ya fita daga jam’iyar ne bisa raɗin kansa.
A ƙarshe ya godewa jam’iyar kan damarmakin da ta bashi a lokacin da yake cikinta a matsayin mamba.
Wasu rahotanni dake fitowa daga jihar Kano sun bayyana cewa Gawuna ya ziyarci jagoran Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso a ranar Litinin sai dai har kawo yanzu ba a bayyana jam’iyar da zai koma ba.

