
Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya kai ziyarar ta’aziya gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai wanda Allah Ya yi wa mahaifiyarsa rasuwa a kasar Masar.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa marigayiyar ta rasu a ranar 27 ga watan Maris ta na da shekaru 96 a duniya bayan da ta yi fama jinya.
Shettima ya kai ziyarar ta’aziyar ne a gidan El-Rufai dake Abuja inda ya yi kira kana samu haɗin kan ƙasa ba tare da duba batun ɓangaren siyasa ba .
Ya yi addu’ar Allah Ya jikanta da rahama.
Tsohon gwamnan jihar Bauchi, Ahmad Adamu Muazu da kuma tsohon babban hafsan sojan Najeriya, Abdulrahaman Dambazau.

