Shettima Ya kai wa El-Rufai ziyarar ta’aziya

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya kai ziyarar ta’aziya gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai wanda Allah Ya yi wa mahaifiyarsa rasuwa a kasar Masar.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa marigayiyar ta rasu a ranar 27 ga watan Maris ta na da shekaru 96 a duniya bayan da ta yi fama jinya.

Shettima ya kai ziyarar ta’aziyar ne a gidan El-Rufai dake Abuja inda ya yi kira kana samu haɗin kan ƙasa ba tare da duba  batun ɓangaren siyasa ba .

Ya yi addu’ar Allah Ya jikanta da rahama.

Tsohon gwamnan jihar Bauchi, Ahmad Adamu Muazu da kuma tsohon babban hafsan sojan Najeriya, Abdulrahaman Dambazau.

More from this stream

Recomended