Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya koma jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a ranar Litinin, matakin da masu lura da siyasa ke kallon a matsayin wani muhimmin sauyi a bangaren ‘yan adawa a Najeriya.
Rahotanni sun nuna cewa shugaban jam’iyyar na ƙasa, David Mark, ya tarɓi Kwankwaso tare da magoya bayansa a gidansa da ke Abuja. Ya bayyana cewa shigar Kwankwaso jam’iyyar ba sauya sheka ba ne kawai, illa yana nuna bukatar da ‘yan Najeriya ke da ita ta ganin an samu haɗin kan ‘yan adawa mai ƙarfi domin kare dimokuradiyya.
Mark ya ce jam’iyyar ADC na ƙoƙarin zama wata dandalin haɗin kai da ke ginuwa a kan gaskiya, ƙwazo da ci gaba, tare da manufar bai wa ‘yan ƙasa zaɓuɓɓuka masu inganci da kuma samun amincewa ga tsarin dimokuradiyya.
Kwankwaso Ya Koma ADC Bayan Ficewarsa Daga NNPP

