Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar bayan shafe kusan shekara huɗu yana cikinta.
Matakin nasa na zuwa ne a daidai lokacin da manyan jiga-jigan adawa a Najeriya ke ƙoƙarin kafa wata haɗakar siyasa da nufin “kawar da jam’iyyar APC a 2027”.
Tsohon gwamnan jihar Kano ya bayyana cewa ya yanke shawarar barin NNPP ne bisa la’akari da yadda siyasar ƙasar ke gudana a halin yanzu, inda ya ce akwai bukatar a samu haɗin kai domin cimma sauyi.
“Matakin ya zama tilas domin haɗa kai da wasu jam’iyyun don kawo wa ƙasarmu sauyi nagari”, kamar yadda Kwankwaso ya bayyana.
Ya kuma miƙa godiya ga magoya bayansa da shugabannin jam’iyyar daga matakin mazaɓa zuwa na ƙasa, bisa damar da ya ce sun ba shi a tsawon lokacin da ya yi a cikin NNPP.
Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP, Ya Nuna Bukatar Haɗin Kan Ƴan Adawa

