Tinubu Ya Miƙa Ta’aziyya Ga El-Rufai Kan Rasuwar Mahaifiyarsa

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya aika saƙon ta’aziyya ga tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, bisa rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Umma.

Rahotanni sun ce Hajiya Umma ta rasu ne a ranar Juma’a a birnin Cairo bayan fama da rashin lafiya.

A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya yabawa rayuwar marigayiyar tare da jajanta wa iyalanta.

Shugaban ƙasar ya bayyana cewa rasa uwa na daga cikin abubuwan da suka fi radadi, yana mai fatan cewa tunanin ƙauna, hikima da tarbiyyar da ta bari za su zama abin kwantar da hankali ga iyalan.

More from this stream

Recomended