Sojojin Isra’ila sun tabbatar cewa harin makamai masu linzami daga Iran ya janyo mummunar ɓarna a yankunan tsakiyar ƙasar, inda aka tura jami’an ceto da agaji zuwa wuraren da abin ya shafa.
Hotunan da hukumomin agajin gaggawa na Isra’ila suka wallafa a shafin Telegram sun nuna hayaƙi na tashi daga gine-gine tare da tarkace da suka bazu a wuraren.
A baya an ruwaito cewa, bayan gargadin da sojojin Isra’ila suka bayar game da yiwuwar harba makamai masu linzami daga rundunar juyin juya halin Iran (IRGC), an tura jami’an agaji zuwa kudancin ƙasar inda aka samu ɓarna bayan harin ya afku.
Harin Makamai Masu Linzami Daga Iran Ya Haifar Da ɓarna A Isra’ila

