Wani babban jami’i a ma’aikatar harkokin wajen Iran ya tabbatar cewa Iran ta samu bayanai daga Amurka ta hannun masu shiga tsakani, kuma a yanzu haka ana nazarin su a matsayin wata hanya da za ta iya kai ga fara tattaunawa tsakanin ƙasashen biyu.
CBS ta bayyana cewa wannan mataki na iya zama kawai shiri ko share fage kafin fara tattaunawa, kuma har yanzu ba a tabbatar da cewa an fara tattaunawar ko ana gudanar da ita ba.
Wannan na zuwa ne bayan da shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce an gudanar da tattaunawa tsakanin Amurka da Iran kan kawo ƙarshen rikicin, sai dai kakakin majalisar dokokin Iran ya musanta hakan.
Trump ya kuma sake jaddada cewa Amurka na da damar cimma yarjejeniya don dakatar da rikicin, bayan ya sassauta barazanar kai hari kan wuraren makamashin Iran tare da dage shirin kai harin.
Iran Ta Ce Ta Karɓi Bayanai Daga Amurka Kan Yiwuwar Tattaunawa

