Rundunar sojin Isra’ila, IDF, ta bayyana a wani sabon rahoto cewa Iran ta harba makamai masu linzami zuwa ƙasar.
A cewar rundunar, dakarunta na ci gaba da tare waɗannan hare-hare, inda suke kakkaɓo su kafin su isa wuraren da aka nufa.
Tun da farko, rahotanni sun nuna cewa an ji ƙarar fashewa a wurare da dama a babban birnin Iran, Tehran.
Haka kuma, an ruwaito cewa an dakile wani sabon jerin hare-haren Iran a birnin Tel Aviv a cikin dare.
Isra’ila Ta Ce Iran Ta Harba Mata Sabbin Makamai Masu Linzami

