
Philips Tanimu Aduda, tsohon sanatan birnin tarayya Abuja ya fice daga jam’iyar PDP.
A wata wasika mai dauke da kwanan watan 17 ga watan Maris da ya aike da ita zuwa ga shugaban mazaɓarsa ta Karu a karamar hukumar AMAC ta birnin tarayya Abuja ya ce murabus din nasa daga jam’iyar ya fara aiki nan take.
Aduda ya wakilci mazabar birnin tarayya a majalisar dattawa daga shekarar 2011 ya zuwa 2023.
Tsohon sanatan wanda na hannun daman Nyesom Wike ne ya alakanta fitarsa daga jam’iyar da rikicin da ya dabaibaye jam’iyar ta PDP.
Ya bayyana godiyarsa ga jam’iyar PDP kan damarmakin da ta bashi na rike mukamai a mataki daban-daban.

