Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai hari a ƙauyen Wanka da ke gundumar Keram, ƙaramar hukumar Kanam a jihar Plateau, inda suka kashe sojoji uku da kuma ’yan sa-kai bakwai.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin ranar Juma’a, lokacin da ’yan bindigar suka mamaye ƙauyen tare da buɗe wuta kan jama’a, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici.
Wata majiya daga cikin al’ummar yankin ta shaida wa manema labarai cewa daga cikin waɗanda aka kashe akwai hafsoshin rundunar soji biyu masu muƙamin kyaftin.
Majiyar ta ce kafin harin, al’ummar yankin sun daɗe suna rayuwa tare da ’yan bindigar, inda suka bayyana cewa sun kusan mamaye yankin gaba ɗaya, suna zuwa su yi abin da suka ga dama sannan su tafi ba tare da korar mazauna ba.
A safiyar ranar Juma’a, jami’an tsaro ƙarƙashin jagorancin kyaftin ɗin biyu sun kai farmaki kan ’yan bindigar, inda suka kashe da dama daga cikinsu yayin da wasu suka tsere.
Sai dai bayan wasu sa’o’i, kuma kafin sojojin su bar yankin, ’yan bindigar sun sake haɗuwa daga cikin dazuka da ke kusa, suka kai wani sabon hari kan sojojin da ’yan sa-kai da ke taimaka musu, lamarin da ya yi sanadin asarar rayuka daga ɓangarorin biyu.
‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji Uku Da ’Yan Sa-Kai Bakwai A Jihar Plateau

