Amurka Ta Yi Iƙirarin Raunata Sabon Jagoran Addinin Iran

Sakataren tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya bayyana cewa an raunata jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, kuma akwai yiwuwar an illata shi. Sai dai editan labaran ƙasashen waje na BBC ya ce ba a tabbatar da hakan ba.

Hegseth ya yi wannan iƙirari ne lokacin da ya kafa hujja kan sanarwar da Mojtaba ya fitar a ranar Alhamis, wadda aka watsa a gidan talabijin na gwamnatin Iran. Ya ce ba a ga bidiyon Mojtaba ba, sannan ya ƙara da cewa, “Na san kun san me ya sa.”

Sakataren tsaron Amurka ya ƙara da cewa Mojtaba na cikin “tsoro” kuma an raunata shi.

More from this stream

Recomended