Gwamnan Sokoto Ya Umarci A Biya Ma’aikata Albashin Maris Kafin Sallah


Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya bayar da umarnin a biya ma’aikatan jihar albashinsu na watan Maris domin su samu damar gudanar da bikin ƙaramar Sallah cikin sauƙi.

Sanarwar da daraktan yaɗa labaran gwamnan, Abubakar Bawa, ya fitar a yau Talata ta ce gwamnan ya ɗauki matakin ne domin tabbatar da jin daɗin ma’aikatan jihar.

Sanarwar ta ce, “tun bayan zuwan wannan gwamnati take tabbatar da cewa an biya ma’aikata albashi a kan kari”.

Haka kuma ta bayyana cewa gwamnan ya biya bashin kuɗaɗen giratuti da ya gada daga gwamnatin da ta gabata.

Gwamna Ahmed Aliyu ya buƙaci ma’aikatan jihar da su mayar da hankali wajen gudanar da ayyukansu domin su saka wa gwamnatin jihar da kyakkyawan aiki.

More from this stream

Recomended