
Ipalibo Banigo sanata dake wakiltar mazabar yammacin jihar Ribas ta sauya sheka daga jam’iyar PDP ya zuwa APC.
Shugaban majalisar dattawa, Godswil Akpabio shi ne ya sanar da haka a yayin zaman majalisar na ranar Talata lokacin da yake karanta wasikar da ta aikewa shugabancin majalisar.
A cikin wasikar sanatan ta ce ta ɗauki matakin ne bayan tuntubar mutanen mazaɓarta da kuma abokanan siyasarta.
“Na rubuto domin na sanar da kai da kuma sauran masu girma abokan aikina a majalisar dattawa kan matakin sauya sheka daga jam’iyar PDP da kuma komawa jam’iyar APC,” a cewar wasikar.
Banigo ta ce ta fice daga jam’iyar PDP ne sakamakon rikicin cikin wani gida da ya dabaibaye jam’iyar PDP.

