Jami’an Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) sun kama wani da ake zargin babban kwamandan kungiyar Eastern Security Network (ESN) ne, Sabastine Odo Odam, tare da Ejike Daniel, wanda ake zargin mamba ne na kungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB).
Rahotanni sun ce an kama mutanen biyu ne ranar Juma’a, 6 ga watan Maris, a yankunan Eha-Amufu da Umuhu da ke karamar hukumar Isi-Uzo a jihar Enugu.
Masani kan harkokin tsaro, Zagazola, ne ya bayyana hakan ta shafinsa na X, inda ya ce majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa an kama su ne bayan watanni na tattara bayanan sirri kan ayyukan da ake zargin suna aikatawa.
Majiyoyin sun ce kamen ya biyo bayan hare-hare da dama da aka kai kan ofisoshin ‘yan sanda da kuma kashe-kashen da suka faru tsakanin shekarar 2024 zuwa 2026 a karamar hukumar Isi-Uzo.
Jami’an DSS Sun Kama Wani Babban Kwamandan ESN Da Wani Da Ake Zargin Dan IPOB Ne A Enugu

