Wani jirgin ruwa mallakin kamfanin Faransa ya tsallaka mashigar Hormuz bayan samun izinin Iran, inda aka tabbatar da cewa ya wuce lafiya ba tare da wata matsala ba.
Rahotanni sun ce jirgin ya taso ne daga kusa da Dubai a Hadaddiyar Daular Larabawa kafin ya nufi gabar tekun Oman ta mashigar Hormuz.
Ministan sufuri na Faransa, Philippe Tabaro, ya yaba da izinin da Iran ta bayar, yana mai cewa jirgin na ɗauke da tutar Faransa tare da ma’aikatan ƙasar Faransa.
A gefe guda, Oman ta sanar da kirkirar wata sabuwar hanyar ruwa a yankinta. Sai dai Iran ta ce hanyarta ce kaÉ—ai mai aminci, tare da gargadin daukar mataki kan duk jirgin da ya karya umarninta.
Jirgin Ruwan Faransa Ya Tsallaka Mashigar Hormuz Cikin Aminci

