APC Ta Lashe Dukkan Zaɓukan Ƙananan Hukumomin Gombe

Jam’iyyar APC mai mulki a jihar Gombe ta lashe dukkan zaɓukan ƙananan hukumomi 11 da aka gudanar a ranar Asabar 27 ga watan Yuni.

Shugaban hukumar zaɓen jihar, Abdullahi Garba, ya bayyana cewa APC ta samu nasara a dukkan kujerun shugabannin ƙananan hukumomi da kuma kujerun kansiloli 240 na jihar.

Ya bayyana zaɓen a matsayin babban ci gaba, musamman bayan faɗaɗa ƙananan hukumomin jihar zuwa gundumomin mulki 24.

A Najeriya, galibi jam’iyyar da ke mulkin jiha ce ke samun rinjaye a zaɓukan ƙananan hukumomi.

More from this stream

Recomended