Rundunar sojin Amurka mai kula da yankin tsakiya, CENTCOM, ta sanar da kai hare-hare kan Iran bayan wani hari da aka kai wa jirgin kasuwanci a mashigar Hormuz.
CENTCOM ta bayyana cewa harin martani ne ga abin da ta kira harin da Iran ta kai wa jirgin ruwa ranar Alhamis, wanda ta ce ya saba wa yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin kasashen biyu.
A wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce, “The unwarranted aggression against commercial shipping by Iranian forces clearly violated the ceasefire.”
Shugaban Amurka Donald Trump ma ya zargi Iran da kai harin, inda ya bayyana shi a matsayin “a foolish violation” na yarjejeniyar tsagaita wuta.
Rahotanni sun ce babu wanda ya rasa ransa bayan jirgin ya gamu da hari ta jirgin sama mara matuki.
Wannan ne karo na farko da aka samu irin wannan martani tsakanin kasashen biyu tun bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da ta kawo karshen rikicin da ke tsakaninsu a makon da ya gabata.
Har yanzu Iran ba ta musanta ko amincewa da hannu a harin ba, sannan ba ta fitar da wata sanarwa kan hare-haren da Amurka ta kai mata ba.
Ana ci gaba da tattaunawa tsakanin kasashen biyu a Switzerland domin samar da zaman lafiya mai dorewa.
Amurka Ta Kai Hari Kan Iran Bayan Harin Jirgin Ruwa A Hormuz

