Babu jam’iyun Labour Party da PDP a cikin waɗanda za su yi takara a zaben gwamnan Osun

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta fitar da jerin sunayen waɗanda za su yi takara a zaben gwamnan jihar Osun da za a gudanar  ranar 8 ga watan Agustan wannan shekara.

Sai dai kuma babu sunan yan takarar jam’iyyun Labour Party da kuma PDP.

A wata sanarwa da Musa Olurode mai magana da yawun hukumar INEC a jihar Osunya ce yan takara daga jam’iyu 14 aka tantance domin tsayawa takara a zaɓen.

Jam’iyun da za su tsaya sun haɗa da Accord (A), Action Alliance (AA), African Action Congress (AAC), African Democratic Congress (ADC), Action Democratic Party (ADP), All Progressives Grand Alliance (APGA), All Progressives Congress (APC), Allied Peoples Movement (APM), Action Peoples Party (APP), Boot Party (BP), New Nigeria Peoples Party (NNPP), Peoples Redemption Party (PRP), Young Progressive Party (YPP), da kuma  Zenith Labour Party (ZLP).

Olurode ya ce jerin sunayen da aka wallafa shi ne na ƙarshe kamar kamar yadda jadawalin gudanar da zaben ya nuna.

More from this stream

Recomended