Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da bibiyar lamarin Walida Abdulhadi har zuwa ƙarshe domin tabbatar da cewa an yi mata adalci.
Gwamnan jihar, Malam Umar Namadi, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi iyayen Walida tare da lauyansu a gidan gwamnatin jihar. Ya ba su tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar an yi wa ‘yarsu adalcin da ta cancanta.
Ana zargin wani jami’in tsaron farin kaya na DSS da safarar Walida Abdulhadi, inda rahotanni suka ce ta zauna a wajensa har ta haifa masa ɗa a birnin Abuja.
Gwamna Namadi ya ce a halin yanzu Walida tana ƙarƙashin kulawar gwamnatin jihar domin duba lafiyarta da kuma taimaka mata ta farfaɗo da tunaninta.
Ya ce, “Yanzu haka Walida tana ƙarƙashin kulawarmu, ana duba ta domin gyara mata tunani. Daga baya za mu mayar da ita wajen iyayenta.”
Gwamnan ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar za ta tallafa wa Walida da iyayenta domin inganta rayuwarsu.
A cewarsa, “sannan za mu mayar da Walida makaranta mu ɗauki nauyinta domin ta samu ilimi mai kyau.”
Gwamna Namadi ya bayyana abin da ya faru da Walida a matsayin safara, inda ya jaddada cewa gwamnati za ta bi hanyoyin doka domin tabbatar da an yi mata adalci.
Ya ce, “sannan duk wanda aka samu da hannu a lamarin dole zai fuskanci hukuncin da ya dace.”
Gwamnan ya kuma nanata kudirin gwamnatin Jigawa na kare ‘yanci da mutuncin ‘yan jihar a duk inda suke.
A nasa bangaren, lauyan iyayen Walida, Barista Kabiru Adamu, ya gode wa gwamnan bisa sa bakin da ya yi wanda ya taimaka wajen ceto Walida.
Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Walida

