
Adewale Egbedun shugaban majalisar dokokin jihar Osun da mambobin majalisar 24 da kuma Moshood Adeoti tsohon sakataren gwamnatin jihar sun koma jam’iyar Accord Party.
Sun kuma bayyana goyon bayansu ga takarar kujerar gwamnan jihar wa’adi na biyu da gwamna , Ademola Adeleke yake a ƙarƙashin jam’iyar ta Accord Party.
A ranar 9 ga watan Disamba 2025 ne Adeleke ya sanar da komawa jam’iyar Accord Party bayan da ya fice daga jam’iyar PDP sakamakon rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyar a matakin ƙasa.
A wata sanarwa, Olamide Tiamiyu mai magana da yawun shugaban majalisar ya sanar da sauya shekar yan majalisar.
Tiamiyu ya ce yan majalisar sun ɗauki matakin sauya shekar ne a wata ganawa da su ka yi inda daga bisani suka wuce dakin taro domin ganawa da gwamnan da kuma jiga-jigan jam’iyar

