Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa kasarsa za ta ci gaba da kai hare-haren bama-bamai masu ƙarfi a Iran ba tare da tsaiko ba a cikin mako mai zuwa.
Trump ya bayyana hakan ne ta wani sako da ya wallafa a dandalin sada zumunta na Truth Social, bayan rahotannin da suka bayyana mutuwar jagoran addinin Iran, Ali Khamenei.
Rahotanni sun ce wannan mataki ya biyo bayan hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kai kan wasu ƙasashen yankin Gulf masu arzikin man fetur, sai dai Oman na taka rawa a matsayin mai shiga tsakani a tattaunawar Amurka da Iran.
Trump Ya Ce Za Su Ci Gaba Da Luguden Wuta A Iran

