Mutane Hudu Sun Mutu, 18 Sun Jikkata Yayin Raba Zakkar Ramadan A Katsina

Akalla mutane hudu sun rasa rayukansu, yayin da wasu 18 suka jikkata sakamakon turmutsitsi da ya faru lokacin raba Zakkar Ramadan a cikin birnin Katsina.

Masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya bayyana lamarin a ranar Asabar ta shafinsa na X, inda ya ce al’amarin ya faru da misalin karfe 9 na dare a ranar Alhamis a gidan Alhaji Dahiru Usman Sarki da ke unguwar Kofar Guga.

Rahotanni sun nuna cewa jama’a da dama sun taru domin karbar tallafin Ramadan, amma wasu sun kutsa kai cikin gidan da karfi, lamarin da ya haddasa turmutsitsi.

Jami’in ‘yan sanda na yankin, DPO na Central Police Station a Katsina, ya tura jami’ai cikin gaggawa zuwa wurin, inda aka samu nasarar shawo kan lamarin.

Mutane 18 sun samu raunuka daban-daban, inda aka kai su General Hospital Katsina domin samun kulawa.

Hukumar ‘yan sanda ta tabbatar da cewa an gayyaci masu shirya rabon zakka domin yi musu tambayoyi, yayin da bincike kan lamarin ke gudana.

More from this stream

Recomended