Gwamnan Zamfara Ya Gana Da Shugabannin Tsaro Kan Yawaitar Hare-Haren ’Yan Bindiga

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gana da shugabannin hukumomin tsaro a ranar Juma’a, sakamakon karuwar hare-haren ’yan bindiga a fadin jihar.

An gudanar da taron ne a gidan gwamnati da ke Gusau, inda aka tattauna kan yadda za a dakile matsalar tsaro da ke kara tsananta.

Wannan na zuwa ne bayan wani hari da ya faru a ranar 21 ga Fabrairu, inda aka ruwaito cewa sama da mutum 50 suka rasa rayukansu a ƙananan hukumomin Anka da Bukuyum.

Har yanzu ba a fitar da cikakken bayani kan sakamakon taron ba, amma ana sa ran za a kara ƙaimi wajen magance hare-haren da ke addabar jihar.

More from this stream

Recomended