Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya haɗu da ’yan majalisar wakilai domin buɗe-baki a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja a ranar Juma’a.
Cikin manyan baƙin da suka halarci taron akwai mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, tare da wasu fitattun jami’an gwamnati.
Taron ya kasance wata dama ta ƙarfafa dangantaka tsakanin ɓangarorin gwamnati a wannan lokaci na azumin watan Ramadan.
Tinubu Ya Shirya Liyafar Buɗe-Baki Da ’Yan Majalisar Wakilai A Abuja

