
Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya kawar da dukkan zargin da ake cewa akwai wani shiri na sauya sheka daga jam’iyar PDP.
Da yake magana da manema labarai a fadar shugaban ƙasa bayan wata ganawa da ya yi da shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu a ranar Juma’a, Ƙauran na Bauchi ya ce tattaunawar da su ka yi tamayar da hankali kan batun mulki da kuma haɗa kai don tunkarar matsalar tsaro.
Gwamnan ya bayyana cewa babu tushe bare makamai a hasashen da ake yi cewa ziyarar ta sa na da alaƙa da fita daga jam’iyar PDP.
“Ni ɗan PDP ne. Ba nazo nan bane saboda siyasa ko sauya sheka na zo nan ne domin batun mulki da kuma haɗa hannu da ƙarfe, ” ya ce.
Muhammad ya ce ya zo ne domin sanar da shugaban ƙasa yadda sha’anin tsaro ya taɓarɓare a ƙaramar hukumar Alkaleri dake jihar inda ayyukan yan bindiga su ka karu saboda dazukan da babu mutane musamman a wajejen madatsar ruwa ta Daji.
Ya ce shi da kansa ya ziyarci wuraren da abun ya shafa tare da shugabannin hukumomin tsaro inda suka duba halin da al’ummar su ke ciki tare da tattara cikakken rahoto domin su ne mu buƙatar daukin gwamnatin tarayya.
Gwamnan ya ce shugaban ƙasa ya amsa rokon nasa inda ya bayar da umarnin gaggauta taimakawa.

