Rundunar Ƴansanda ta Jihar Kebbi ta tabbatar da cewa an kashe masallata biyar a wani hari da aka kai wa masallaci a karamar hukumar Maiyama ta Jihar Kebbi.
Kakakin rundunar, Bashir Usman, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 8:30 na dare a garin Dadin Kowa yayin sallar Taraweeh. Ya bayyana cewa ana zargin ‘yan kungiyar Lakurawa ne suka kai harin.
Ya ce mutane biyar sun mutu, yayin da uku suka jikkata kuma suna karbar magani a asibiti.
Rundunar ta ce maharan sun tsere zuwa daji kafin isowar jami’an tsaro, inda aka tura jami’ai tare da hadin gwiwar sojoji da ‘yan sa-kai domin dawo da zaman lafiya.
Ta kuma mika ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasu da al’ummar yankin.
Ƴan Sanda Sun Tabbatar Da K¡san Masallata Biyar A Kebbi

