Shugaba Tinubu Ya Amince Da Gyare-gyaren Wasu Manyan Hanyoyin Gwamnatin Tarayya

Bola Ahmed Tinubu ya amince da fara gyaran wasu manyan hanyoyi uku na tarayya a Jihar Neja, tare da tsawaita hanyar Bodo–Bonny a Jihar Rivers.

An yanke wannan hukunci ne bayan ganawar shugaban kasa da Ministan Ayyuka, David Umahi.

Hanyoyin da za a gyara sun hada da Mokwa–Bida, Mokwa–Makeri da kuma Bida–Labata. Za a yi aikin ne da siminti mai karfi domin tabbatar da dorewa.

Haka kuma za a tsawaita hanyar Bodo–Bonny domin ta hade da East–West Road, tare da ginawa a matsayin hanya mai bangarori biyu da kuma hasken rana.

More from this stream

Recomended