An kama mutumin da ake zargi da sace mahaifinsa a Jihar Adamawa

Jami’an tsaro a Jihar Adamawa sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a sace wani dattijo a ƙaramar hukumar Fufore, ciki har da ɗansa na jini.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Suleiman Yahaya Nguroje, ya ce kamen ya biyo bayan sace Alhaji Ahmadu da aka yi ranar 30 ga Janairu, 2026 a unguwar Malabu.

A cewarsa, jami’an ’yan sanda sun gudanar da samame ne bisa umarnin Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar domin ƙara tsaurara yaƙi da masu aikata laifuka.

Ya bayyana cewa an kai farmaki wani wuri da ake zargin maboyar masu garkuwa da mutane ne a ƙauyen Jera, tare da haɗin gwiwar jami’an tsaron Miyetti Allah, inda aka kama waɗanda ake zargi.

Waɗanda aka cafke sun haɗa da Lawali Haruna mai shekara 45, Yahaya Ibrahim mai shekara 25, da Da’u Alhaji Ahmadu mai shekara 28, wanda aka tabbatar ɗan wanda aka sace ne.

Rundunar ta bayyana lamarin a matsayin mai tayar da hankali, tana mai cewa dukkan waɗanda aka kama sun amsa zargin da ake yi musu.

Ta ƙara da cewa ana ci gaba da ƙoƙarin kuɓutar da wanda aka sace lafiya tare da kamo sauran ’yan ƙungiyar, yayin da bincike ke gudana. Haka kuma, rundunar ta buƙaci jama’a su ci gaba da ba ta sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaƙi da miyagun laifuka a faɗin jihar.

More from this stream

Recomended