Biyu Daga Cikin Masu Takarar Shugabancin Majalisar Wakilai Sun Janyewa Tajuddeen Abbas

Mutane biyu dake takarar shugabancin majalisar wakilai ta tarayya Aliyu Betara da Yusuf Gagdi sun janye takararsu inda suka goyi bayan Tajuddeen Abbas wanda shi ne ɗantakar da jam’iyar APC ta tsayar.

Betara da Gagdi sun amince sun janye takarar ta su bayan sun gana da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima a ranar Lahadi.

A kwanakin baya ne jam’iyar APC ta fitar da sunan Abbas da kuma Benjamin Kalu a matsayin wanda za su jagoranci shugabancin majalisar wakilai ta 10.

Wasu daga cikin ƴaƴan jam’iyar ta APC ciki har da mataimakin shugaban majalisar, Idris Wase sun ki amincewa da zabin na Abbas.

Da yake magana bayan ganawar, Shettima ya yaba musu kan janye war da suka yi inda ya ce shugaban ƙasar ya ji dadin matuka da janyewar ta su.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]