Hare-hare sun yi sanadiyyar mutuwar mutum sama da dubu cikin wata 4

Wata kungiya mai zaman kanta da ke mai da hankali kan kare hakkin dan Adam da samar da zaman lafiya, Stefanos Foundation, ta bayyana cewa tsakanin watan Janairu zuwa Afrilu, 2023, an kai hare-hare 217 a jihohi 34 na Najeriya.

A cewar kungiyar kare hakkin bil’adaman da ke Jos, hare-haren sun yi sanadiyar mutuwar mutane 1,872, an yi garkuwa da mutane 714, sannan mutane 65 sun samu raunuka daban-daban.

Ms. Fatima Njoku, Manajar wani sashe a gidauniyar Stefanos, a yayin wata ganawa da manema labarai na hadin gwiwa a Abuja ranar Alhamis, ta jaddada cewa akwai bukatar a dauki matakin gaggawa don magance musabbabin tashe-tashen hankula a sassan kasar nan.

Ta ce, “Daga rahotannin gani da ido kuma shaidar wadanda abin ya shafa kai tsaye, muna iya cewa ana kai hare-haren ne a zahiri iri ɗaya, tare da maharan sanye tufafi iri ɗaya cikin salo daya.”

“Hakan ya faru ne a Agatu, Guma, Logo a jihar Benue, Kagoro, Zangon Kataf, Kajuru, Kafanchan a kudancin Kaduna, Bassa, Riyom, Barkin Ladi, yanzu Mangu a jihar Filato, kuma ana ci gaba da jerin gwano”.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]