Hare-hare sun yi sanadiyyar mutuwar mutum sama da dubu cikin wata 4

Wata kungiya mai zaman kanta da ke mai da hankali kan kare hakkin dan Adam da samar da zaman lafiya, Stefanos Foundation, ta bayyana cewa tsakanin watan Janairu zuwa Afrilu, 2023, an kai hare-hare 217 a jihohi 34 na Najeriya.

A cewar kungiyar kare hakkin bil’adaman da ke Jos, hare-haren sun yi sanadiyar mutuwar mutane 1,872, an yi garkuwa da mutane 714, sannan mutane 65 sun samu raunuka daban-daban.

Ms. Fatima Njoku, Manajar wani sashe a gidauniyar Stefanos, a yayin wata ganawa da manema labarai na hadin gwiwa a Abuja ranar Alhamis, ta jaddada cewa akwai bukatar a dauki matakin gaggawa don magance musabbabin tashe-tashen hankula a sassan kasar nan.

Ta ce, “Daga rahotannin gani da ido kuma shaidar wadanda abin ya shafa kai tsaye, muna iya cewa ana kai hare-haren ne a zahiri iri ɗaya, tare da maharan sanye tufafi iri ɗaya cikin salo daya.”

“Hakan ya faru ne a Agatu, Guma, Logo a jihar Benue, Kagoro, Zangon Kataf, Kajuru, Kafanchan a kudancin Kaduna, Bassa, Riyom, Barkin Ladi, yanzu Mangu a jihar Filato, kuma ana ci gaba da jerin gwano”.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...