Gwamnan Taraba Ya Durkusa Har Ƙasa Ya Na Neman Al’umma Su Yafe Masa

Gwamnan jihar Taraba, Darius Ishaku ya nemi afuwar mutanen Taraba h waɗanda ya batawa a tsawon wa’adinsa na shekara 8.

Ishaku ya nemi ayi masa afuwa ne yayin taron addu’ar nuna godiya da kungiyar Kiristoci ta CAN reshen jihar Taraba ta shirya a hedkwatar ta dake Jalingo.

Gwamnan ya ce yayi murna cewa takensa na ” Ku bani Zaman Lafiya Ni Kuma Zan Kawo Muku Ayyukan Cigaba.” ya samu wurin zama a zukatan al’ummar jihar.

Tun da farko Ishaku a wurin taron addu’o’in Bikin Ista na musamman da aka gudanar a Cocin Anglican dake Mayo Dosa a Jalingo ya durkusa har ƙasa a gaban mahalarta taron inda ya nemi gafarar mutanen da ya batawa a cikin shekaru 8 na mulkinsa.

Za a iya cewa Gwamna Ishaku ya bi sawun shugaban kasa Muhammad Buhari da kuma gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje da suka nemi jama’a su ya fesu

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]