Muhammadu Buhari: Shugaban Najeriya ya ki amincewa da zaben ‘yar tinke

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ki sanya hannu a kan kudurin dokar da ‘yan majalisar dokoki suka amince da shi domin yin garambawul ga dokar zabe ta 2021.

A wasikar da shugaban ya rubuta wa Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmed Lawan, ya ce irin matsalolin da kasar ke fuskanta ya sa ba zai sanya hannu kan kudurin ba.

Daga cikin dalilan da ya zayyana a wasikar, Shugaba Buhari ya ce zunzurutun kudin da zaben ‘yar tinke zai ci, da kuma kalubalen tsaro da za a fuskanta wurin gudanar da shi na daga cikin abubuwan da ya duba da suka hana shi saka wa kudurin hannu.

Haka ma ya yi batun hakkin da ‘yan kasa suke da shi da kuma ware kananan jam’iyyu daga tafiyar.

Dama batun zaÉ“en fid da gwani ta hanyar ‘yar tinÆ™e, shi ne babban abin da ya janyo taÆ™addama a gyaran-fuskar da aka yi wa dokar zaÉ“en.

Tun da farko wasu daga cikin ‘yan majalisar sun sha alwashin aiki da ikon da kundin tsarin mulkin kasa ya ba su, na tabbatar da dokar ko da shugaban bai sa mata hannu ba.

Sai dai dai a yanzu za a iya cewa lamarin ya sauya salo, kuma matakin na shugaban kasa ba lalle ya yi wa da dama daga cikin ‘yan majalisar dadi ba.

To amma kuma Shugaba Muhammadu Buhari ya jaddada wa majalisar cewa ba ya yi gaban kansa ba ne wurin daukar wannan mataki.

Don a cikin wasikar ya fadi cewa ya nemi shawarwari daga ma’aikatun da ke da ruwa da tsaki a harkar, ya kuma yi nasa nazarin la’akari da halin da kasar ke ciki.

Hakan ya sa a karshe ya ga cewa abu mafi dacewa shi ne a kyale jam’iyyu su zabi yadda suke so su gudanar da zaben fid da gwanayen da za su tsaya musu takara.

Tun farko wasu ‘yan majalisar sun fara kunfar baki bayan da suka ji shiru daga Shugaban kasar, yayin da wa’adin da yake da shi na sanya wa kudurin dokar hannu ya wuce.

Hakan ta sa wasu daga cikin wakilan al’ummar sha alwashin aiki da ikon da kundin tsarin mulkin kasa ya ba su, na tabbatar da dokar ko da shugaban bai sa hannu ba.

To amma yanzu kallo zai koma ga ‘yan majalisar domin jin martaninsu, ganin cewa fadar Shugaban kasar ta bayyana matsayarta kan dokar zaben.

Wasu na zargin gwamnonin Najeriyar da kai komo fadar Shugaban kasar don ganin cewa Shugaba Muhammadu Buhari bai amince da garambawul din ba.

Masu sharhin siyasa na ganin cewa kin saka hannu da Shugaban kasar ya yi mataki ne da zai yi wa gwamnonin dadi, don ana zargin cewa da dama daga cikinsu ba sa goyon bayan zaben ‘yar tinke wurin tsayar da ‘yan takara a jihohinsu.

A daya bangaren kuma ‘yan majalisa na ganin zaben ‘yar tinken hanya ce da za ta kawo wa gwamnonin cikas, a babakeren da ake ganin suna yi wurin tsayar da ‘yan takara.

More News

Ruwan Sama Da Iska Sun Rusa Gidaje Sama Da 200 A Katsina

Akalla gidaje sama da 200 ne suka rushe sakamakon ruwan sama mai tafe da iska mai ƙarfi da ya afku a ƙaramar hukumar Kusada...

Yan bindiga sun yi garkuwa da alkalin babbar kotun jihar Kebbi

Yan bindiga sun yi garkuwa da Faruk Hassan Bunza alkalin babban kotun jihar Kebbi. An yi awon gaba da alkalin ne da tsakar daren  ranar...

An kama sojan dake sayarwa da yan ta’adda kakin soja

Rundunar sojan Najeriya ta samu nasarar kama wani sojanta da ta sanar tana nema ruwa a jallo bayan da aka zarge da laifin sayarwa...

Mutane Da Dama Sun Jikkata Bayan Mota Ta Kutsa Cikin Taron LGBT A Berlin

Mutane da dama sun samu raunuka bayan wata mota ta kutsa cikin taron masu goyon bayan LGBT a birnin Berlin na ƙasar Jamus.Rahotanni sun...