
Hakkin mallakar hoto
@JIDESANWOOLU
Kwana 100 da ɓullar cutar korona Najeriya, annobar wadda aka fara gano ta ranar 27 ga watan Fabrairu, a jikin wani baturen ƙasar Italiya, zuwa yanzu ta harbi mutane kimanin 12,233 a ƙasar.
Alƙaluman da hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa ta fitar a daren Asabar sun nuna cewa a cikin kwana 100, korona ta kashe mutum 342 a Najeriya.
Haka zalika annobar ta ɓulla a kusan dukkan jihohin ƙasar, ciki har da babban birnin ƙasar, in ban da Cross river.
Yawan alƙaluman masu cutar da hukumar NCDC ke fitarwa a kullum ya ƙaru, mai yiwuwa saboda haɓaka gwaje-gwajen da hukumomin ƙasar suka yi.
Alƙaluma na baya-bayan nan da hukumar ke fitarwa na zuwa cikin adadin ɗaruruwa.
Ko a ranar Asabar 30 ga watan Mayu, hukumar ta ba da rahoton gano mutum 553 da cutar ta sake harba cikin sa’a 24, ba a dai taɓ samun adadi mai yawan haka ba cikin kwana guda a ƙasar.
Haka zalika, kusan rabin mutanen da aka gano sun kamu na cikin jihar Legas, inda cutar ta fara ɓulla. Yanzu dai alƙluman hukuma sun ce akwai masu korona 5,729 a jihar.
Hakkin mallakar hoto
@JIDESANWOOLU
Daga ita sai jihar Kano, wadda cutar ta fara bayyana cikinta ranar Asabar 11 ga watan Afrilu. Yawan masu korona a Kano zuwa yanzu ya kusa mutum 1,000.
A baya-bayan nan ƙwararru sun bayyana damuwa kan ƙarancin gwajin da ake samu a Kano, suna cewa cutar na daɗa fantsama cikin jama’a kuma ta hanyar gwaji da killace masu cutar ne kawai za a iya shawo kanta.
Gwamnatin Kano dai ta ce za ta ƙara ƙimi ta hanyar bin gida-gida wajen gudanar da aikin gwaji a jihar.
Ranar 23 ga watan Maris ne kusan wata ɗaya da fara ɓullar cutar a Legas, aka ba da rahoton samun mutum na farko da ya fara kamuwa da korona a Abuja.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasar, Atiku Abubakar ya sanar ta hanyar wani saƙon tiwita cewa ɗansa, Mohammed Atiku ya kamu har ma an kwantar da shi a asibitin Gwagwalada.
Ko da yake a cikin wani saƙon bidiyo da ya taɓa fitarwa daga inda yake jinya, Mohammed Atiku ya ce tun ranar Juma’a 20 ga wata, aka tabbatar masa cewa cutar ta harbe shi
Mohammed Atiku dai na daga cikin mutanen da suka fi daɗewa suna jinyar korona a cibiyar killacewa, kafin sallamo shi bayan ya shafe kimanin kwana 40 yana jinya.
Shi da fitattun mutane kamar Gwamna Nasir elrufa’i na Kaduna da takwaransa na Bauchi, Bala Mohammed da Seyi Makinde na Oyo duk sun yi fama da cutar a tsawon wannan lokaci kuma sun warke.
Haka zalika a tsawon wannan lokaci an samu jihohi irinsu Zamfara da Kebbi, waɗanda suka ce sun sallami duk masu cutar da aka kwantar a cibiyoyin killacewarsu bayan an tabbatar sun warke.
Hakkin mallakar hoto
Getty Images
Sai dai, bayan kimanin mako guda, an sake samun masu cutar biyu a jihar Kebbi.
A ranar Litinin 23 ga watan Maris ne kuma Hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta sanar da samun mutum na farko da ya rasu saboda cutar korona a Najeriya.
Hukumar NCDC ta ce mutumin ɗan shekara 67 ya dawo Najeriya ne bayan ya je ganin likita Burtaniya, a cewarta mamacin (Injinya Sulaiman A-ci-mugu) ya yi fama da wadansu kwantattun cutuka kafin rasuwarsa.
Hakkin mallakar hoto
Facebook
Engineer Sulaiman ya yi fama da cutar daji da ciwon suga kafin cutar korona ta kama shi
A ranar 7 ga watan Afrilu kuma, Gwamna Masari na jihar Katsina ya sanar cewa Allah Ya yi wa mutum na farko da ya kamu da coronavirus a jiharsa, Dr Aliyu Yakubu rasuwa.
Ya ce likitan wanda ke garin Daura, an ba da rahoton ya yi tafiya zuwa Lagos, kuma bai dade da komawa gida ba, ya kamu da rashin lafiya inda ya kai kansa asibiti kafin cikawarsa.
Cutar korona ta yi sanadin mutuwar Mallam Abba Kyari, shugaban ma’aikatan fadar shugaban Najeriya ranar Juma’a 17 ga watan Afrilu
Abba Kyari ya rasu ne a Legas, inda ya koma jinya bayan ya kamu da cutar ranar 24 ga watan Maris..
Bayanan hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa na cewa jihar Legas ce ta fi yawan masu korona da suka mutu zuwa yanzu da mutum 67.
Daga ita sai jihar Kano, inda Allah Ya yi wa mutum 48 rasuwa sanadin cutar. Jihar Borno, mutum 26 ne suka mutu, in ji alƙaluman NCDC.
A Abuja, mutum 22 ne suka rasu sakamakon cutar zuwa yanzu. Yayin da Katsina kuma aka samu mutuwar masu cutar 20.
Ranar 30 ga watan Maris ne kuma shugaban ƙasar ya fara ɗaukar matakin kulle Najeriya, da nufin shawo kan annobar ta korona.
Har yanzu Najeriya ba ta kai ga buɗe harkokin sufurin jiragen samanta ba, haka kuma matakin hana zirga-zirga tsakanin jihohi na ci gaba da aiki.
Duk da yake, an buɗe wuraren ibada a jihohi da dama da kuma babban birnin ƙasar Abuja, amma har yanzu kasuwanni na ci ne rabi-da-rabi.
Kuma ma, gwamnatin ƙasar ta ce ba ta sa ranar komawa ci gaba da harkokin koyo da koyarwa a makarantun Najeriya ba.