Adadin mutanen da suka mutu a Najeriya ya kai 10 – NCDC

Covid-19

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Hukumar dakile yaduwar cutuka a Najeriya ta ce ya zuwa karfe 9:30 na daren ranar Asabar, an samu karin mutum 13 da suka kamu da coronavirus a kasar.

Wannan na nufin adadin mutanen da suka kamu da cutar a kasar ya kai 318 jimilla.

Hukumar ta ce 11 daga cikin karin mutum 13 na Jihar Legas sai 1 a Delta da kuma daya a Kano – jiha ta baya-bayan nan da cutar ta bulla.

A cewar hukumar, cutar ta covid-19 ta bulla a jihohi 19 cikin 36 da ke kasar kuma kawo yanzu, an sallami mutum 70 daga asibiti sai guda 10 da suka riga mu gidan gaskiya.

  • Lagos- 174
  • FCT- 56
  • Osun- 20
  • Edo- 12
  • Oyo- 11
  • Ogun- 7
  • Bauchi- 6
  • Kaduna- 6
  • Akwa Ibom- 5
  • Katsina-4
  • Delta- 3
  • Enugu- 2
  • Ekiti- 2
  • Rivers-2
  • Kwara- 2
  • Ondo- 2
  • Benue- 1
  • Niger- 1
  • Anambra- 1
  • Kano-1

More from this stream

Recomended