An amince wa dan Ghana ya buga kwallo a Italiya

Emmanuel Agyemang

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Hellas Verona ta sanar da cewar likitoci sun tabbatar da cewar dan kasar Ghana, Emmanuel Agyemang Badu zai iya ci gaba da buga mata tamaula.

A cikin watan Agusta aka kai dan wasan mai shekara 29 asibiti, bayan da bincike ya tabbatar cewar gudan jini ya taru a huhunsa.

Kungiyar ta tabbatar da cewar bayan da kwararrun lafiya suka yi masa aiki, yanzu ya samu sauki zai iya murza-leda.

Dan wasan mallakar Udinese ne, wadda ta bayar da aronsa ga Hellas Verona da yarjejeniyar sayar mata da shi, idan ya taka rawar gani.

Badu bai buga wa tawagar kwallon kafa ta Ghana gasar cin kofin nahiyar Afirka ba da aka yi a Masar, wanda Algeria ta lashe kofin.

Dan wasan ya yi doguwar jinyar wata 11, inda ya koma atisaye cikin watan Maris, dalilin da ya sa Ghana ba ta ba shi goron gayyata ba.

More from this stream

Recomended