2023: Kuna ganin APC za ta tsayar da Bola Tinubu a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa?

Yayin da zaɓen 2023 yake ƙara ƙaratowa, wasu daga cikin ƴan siyasar ƙasar sun fara nuna aniyarsu ta tsayawa takara.

Ɗaya daga ciki shi ne tsohon gwamnan Lagos kuma uban jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu.

Mai karatu zai iya tuna cewa kwanakin baya tsohon gwamnan na Lagos ya faɗa wa Shugaba Muhammadu Buhari cewa yana da aniyar tsayawa takarar shugabancin Najeriya.

Sai dai har yanzu jam’iyyar tasu ba ta fitar da gwani ba, yayin da shi ma tsohon gwamnan Abia, Urzo Kalu, yake nuna muradinsa ga kujerar.

Abin tambaya a nan shi ne, shin APC za ta tsayar da Bola Tinubu a matsayin ɗan takararta?

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]