Ɗan sanda ta kashe kansa a jihar Neja

Shafi’u Bawa wani ɗan sandan kwantar da tarzoma ya kashe kansa a Kantagora ta jihar Neja.

Bawa dake da muƙamin ASP  na aiki ne da  rundunar ƴan sandan kwantar da tarzoma runduna ta 61 an kuma gano shi yana reto ɗaure a igiya a cikin dakinsa da yammacin ranar Asabar.

Mahaifin ɗan sandan shi ne ya fara kwarmata faruwar lamarin bayan da ya gano gawar ɗan nasa inda ya kai rahoton faruwar lamarin ofishin ƴan sanda na Kantagora..

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Wasiu Abiodun mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Neja ya ce  tuni aka fara bincike domin gano musabbabin mutuwar tasa.

Abiodun ya ce tuni aka miƙa gawar marigayin ga ƴan uwansa domin yi masa jana’iza kamar yadda addinin musulunci ya tanada.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]